Skip to main content

Posts

Showing posts from December, 2017

Matsayin Sallah Da Hukuncinta BY MUSA MUHAMMAD MUKTAR

Matsayin Sallah Da Hukuncinta Bayani Mece ce Sallah Ma’anar kalmar sallah a larabce Ita ce «Addu’a» Ma’anar Sallah a shari’ance Ita ce bautawa Allah da zantuka da ayyuka kevantattu, waxanda ake buxe su da kabbara, a rufe su da sallama. Matsayin Sallah A Musulunci 1 – Sallah ita ce rukuni na biyu a rukunan musulunci, Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “An gina musulunci a bisa ginshiqai guda biyar, shaida wa babu abin bauta wa bisa cancanta sai Allah, kuma Muhammad bawansa ne Manzonsa ne, da tsayar da sallah…..” [Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi] . 2 – Sallah ita ce mafi falalar ayyuka, Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “Mafi falalar ayyuka sallah a farkon lokacinta” [ Tirmizi ne ya rawaito shi] . 3 – Sallah ce mararraba tsakanin musulunci da kafirci, Annabi (S.A.W) ya ce, “Haqiqa tsakanin mutum da shirka da kafirci barin sallah” [Muslim ne ya rawaito shi] . 4 – Sallah ita ce ginshiqin musulunci, a kanta ne – bayan tauhidi – aka gina musulunci, Annabi yana cewa “Kan wannan ...

NASIHA AKAN WANDA BAYA SALLAH KO YAKE WASA DA ITA BY MUSA MUHAMMAD MUKTAR

Tsoratarwa Akan Wanda Ba Ya Yin Sallah Ko Yake Wasa Da Ita Tsoratarwa Akan Wanda Ba Ya Yin Sallah Ko Yake Wasa Da Ita Sallah daya ce daga cikin rukunnan musulinci guda biyar wanda musuluncin bawa ba ya cika har ya tsayar da ita. Mazon Allah SAW yana cewa: "Tsakanin mutum da tsakanin shirka da kafirci, shine barin Sallah. (Muslim). Manzon Allah SAW yana cewa: "Alkawarin da yake tsakanin mu da kafurai ita ce sallah, dukkan wanda ya bar sallah to ya kafirta). @ ﺳﻨﻦ ﺍﻟﺘّﺮﻣﺬﻱ ﻭﻏﻴﺮﻩ . Imam Tirmizy ya ruwaito daga Abdillahi bn Shaqeeq al'ukaily yace: "Sahabban Annabi Muhammad s.a.w basu ganin barin aiki wani aiki kafircine inbanda sallah". @ ﺍﻟﺘّﺮﻣﺬﻱ. Wato sun hadu akan dukkan wanda ya bar sallah kafiri ne. Manzon Allah s.a.w yana cewa: "Farkon abinda za'ayi wa bawa hisabi akansa na aiyukansa shine sallah, idan ta cika ta yi kyau ya tsira kuma ya rabauta, idan ba ta yi kyau ba kuma bata cika ba ya halaka ya tabe, idan an sami nakasa a cikin f...

HASSADA MUGUN CIWO , ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA ,( Imam Aliyu Indabawa )

HASSADA MUGUN CIWO , ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA ,( Imam Aliyu Indabawa ) Wannan da kuke gani shine Dr kalifa qaribullah nasiru kabara, wanda ya kasance shine halifan dariqar qadiriyya, kuma muna girmama shi saboda halayensa na kawaici da sanin ya kamata, sai Allah ya jarrabe shi da wani taqadarin kani wanda ya addabe shi da hassada kullum cikin zaginsa yakeyi yana kushe shi yana aibata shi, . Asali abinda yasa yake masa wannan hassadar shine saboda halifa qaribullahi Allah yayi masa ni'imomi da baiwarwaki wanda shi kanin nasa bashi dasu, yafi shi duk wani abu da ake so, ta bangaren daukaka, da Ilmi da 'yaya da kudi da magoya baya da manyan mutane Sarakuna, uwa uba kuma yana da hankali wanda shi kanin nasa yayi rashinsa, . Sannan ga mukamin Halifa da yake rike dashi wanda shine yafi komai kona masa zuciya da motsa masa hassada, saboda shi a tunaninsa ai shine yafi cancanta daya gaji mahaifinsa ya zama halifan qadiriya saboda tunan...

HUDUBAR JUMU' A DAGA MASALLACIN JUMU' A NA IHYA ' US SUNNAH DAKE KOFAR NASSARAWA KANO AUDIO MP 3 ( Basheer Journalist Sharfadi )

HUDUBAR JUMU' A DAGA MASALLACIN JUMU' A NA IHYA ' US SUNNAH DAKE KOFAR NASSARAWA KANO AUDIO MP 3 ( Basheer Journalist Sharfadi ) -A yau Jumu'a 21/Shawwal/1436. Wadda tayi dai-dai da 07/Aug/2015. Babban Limamin Masallacin Jumu'a na Ihya'us-Sunnah dake Kofar Nassarawa a Karamar Hukumar Birnin Kano da Kewaye. Sheik Dr. Muhammad Sani Ashir Kano Shine Ya Jagoranci Huduba da Sallah a Masallacin. -Dr. Sani Ashir Kano ya fara gabatar da Hudubar sa ne da misalin Karfe 12:30 na rana a Masallacin. Inda aka tayar da Sallah da Karfe 01:05 na rana Bayan Kammala Hudubar. Babban Limamin Yayi Hudubar ne Akan Tauhidi wato Kadaita Allah da yi masa bauta shi kadai. -An gudanar da Sallar cikin nutsuwa da kwanciyar Hankali Kamar Yadda aka saba tare da Gudummuwar Yan agaji wajen bayar da da kyakykyawar Kulawa Domin ganin ayyuka sun gudana kamar yadda aka saba. -Kar dai na cikaku da surutu Danna Kasa Domin Sauraron Hudubar daga Bakin Dr.: