Skip to main content

Posts

Showing posts from November, 2017

027- ABUBUWAN DA BA’A YIN SU A SALLAH

Shinfida: Su wadanann abubuwa su malamai suke kira ‘Makruhatus Salah’ wato abubuwan da ba’a so ayi su a cikin sallah, domin yinsu yana matukar ragewa mutum ladan sallarsa, dudda sallar bat abaci ba ta yadda za’a ce sai ya sake, kuma ba zai yi kabaliyyah ko ba’adiyyah saboda ya yisu ba, saboda haka sai a kiyaye kada mutum ya yi wasa da sallarsa, Hssan dan Atiyyah yake cew: ‘’Lalle mutane biyu za su iya kasancewa a cikin sallah guda, amma tazarar dake tsakaninsu na falala ya fi nisan sama da kasa’’. Lalle wannan ba karamar Magana bace indai har mutane biyu za su kasance a sallah guda bayan limami guda amma banbancin dake tsakaninsu ya dara tazarar dake tsakanin sama da kasa, to kan lalle bakaramin banbanci bane, sannan tambaya anan itace: Me ya janyo wannan banbanci na falala?. Natsuwa kwantar da hankali kankar-da-kai, da kuma sanin me mutum yake yi da nisantar abinda ba’a so mutum ya yi a cikin sallah, wadannan kadanne daga cikin abubuwan da za su banbanta falalar masallata, ga kadan...

ABUBUWAN DASUKE BATA SALLAH BY FADEELA ABDUL KAREEM

Gabatarwa: Anan za’a kawo bayanaine na kadan daga cikin abubuwan da suke bata sallah ta yadda ba abinda ya ragewa mutum saidai ya sake wannan sallar, kabaliyyah ko ba’adiyyah basa magance matsalar da aka samu. Wannan ya nuna cewa lalle wannan maudu’i yanada matukar muhimmanci ga kowanne mutum musulmi. Ga kadan daga cikinsu: 1. Dariya: Dariya tana daga cikin manyan abubuwan da suke bata sallah ko an yi ta da gangan ne ko kuma da mantuwa wato ya manta cewar shi yana sallah, ai ba mai dariya a sallah sai rafkananne, saboda haka mu sani sallah ba karamar ibada bace ba’a dariya a cikin sallah kuma duk wanda ya yi dariya a cikin sallah to sallar shi ta baci sai ya sake ta. 2. Kari Dagangan: Idan mutum ya yi Karin raka’a ko ruku’u ko sujjada dagangan to anan sallarsa ta baci, domin kuma ya dauki addinin da wasa da wargi, wanda yake addinin musulunci bai ginu akan hakaba. Amma idan rafkana ya yi har ya yi kari to anan sallar shi bata baciba bayanan yadda zai gyra za su zo ababin kabaliyyah ...

029- SUJJADAR RAFKANNUWA (KABALIYYAH DA BA’ADIYYAH) ›

Gabatarwa: Ayanzu da izinin Allah muna son mu kawo bayanaine da suka shafi sujjar rafkannuwa wacce ake kira Kabaliyyah ko ba’adiyya da fatan Allah ya anfanar da mu da wadannan bayanai, kuma ya sanya ya zama sanadiyyar tsira duniya da lahira. Wadannan bayanai za su kunshi me ake nufi da sujjadar rafkannuwa ko mecece kabaliyyah sannan mecece ba’adiyyah, sannan a kawo bayanai na abinda ke sabbaba wadannan sujjadu. Sujjadar Rafkannuwa: Sujjadune guda biyu da mutum yake yinsu bayan ya kammala sallah kafin sallama ko bayan sallama saboda kari ko ragi ko kokwanto da ya yi a cikin sallah. Wannan ta’arifi da ya gabata ya fayyace mana me ake nufi da sujjadar rafkannuwa kuma ya yi bayanin abinda yasa ake yenta da kuma lokacin da ake yenta da kuma dadi nawa ake yi. Kabaliyyah : Sune sujjadu biyu da ake yi bayan tahiyyah kafin sallama, kasancewa ana yinta kafin sallama shi yasa ake kiranta kabaliyyah wato ‘Kabals Salam’. Ba’adiyyah: Sune sujjadu biyu da ake yi bayan an sallame daga sallah, sa...

030. ABUBUWAN DA SUKE KAWO KABALIYYAH

Gabatarwa: Ayanzu za’a kawo bayanaine akan abubuwan da suke sanya kabaliyyah kadai, sannan bayan haka a kawo bayanai akan abubuwan da suke sanya ba’adiyyah suma su kadai, fatammu a tsaya a karanta bayanan a natse kuma a fahimcesu, idan akwai abninda ya shigewa mutum yana da dama ya yi tambaya, da fatan Allah ya ganar da mu. Abubuwan Da Suke Kawo Kabaliyyah: Manyan abubuwan da ke sawa a yi sujjadar Kabaliyyah su ne; 1. Ragi. 2. Ragi Da Kari.(Alokaci guda) Dukkan mutumin da ya yi ragi a sallar sa to kabaliyyah ta kamashi, kamar: 1. Karatun Sura: Idan mutum ya manta a raka’ar farko ko a ta biyu bai karanta suraba kawai shi da ya karanta fatiha sai ya yi sujjada, to wannan kabaliyyah ta kamashi. 2. Asurtawa A Inda Ake Bayyanawa: Duk wanda ya yi karatun sallah sirrance a inda ake bayyanawa, to wannan shima kabaliyyah ta kamashi. 3. Fadin ‘’Sami’allu Liman Hamidah’’ haka wanda ya manta da fadin wannan kalma kabaliyyah zai yi domin rage. 4. Tahiyar Farko: Duk wanda ya barta to ya yi ...

031. ABUBUWAN DA SUKE KAWO BA’ADIYYAH (1)

Gabatarwa: Ayanzu za’a kawo bayanaine akan abubuwan da suke sanya ba’adiyyah kadai, da fatan Allah ya an fanar da mu. Manyan abubuwan da suke haifar da ba’adiyyah, abubuwane kamar haka: 1. Kari (Da mantuwa) 2. Kokwanto Wadannan sune manyan abubuwan da suke kawo sujjadar ba’adiyyah, kuma akan su za muyi bayani a wannan karon da izinin Allah. Idan mutum ya yi kari a sallah da rafkannuwa ba wai daganganba to ba’adiyyah zai yi, kamar mutumin da ya kara raka’a a asuba ta zama uku, ko a magariba ta zama hudu, ko kuma a azahar ko la’asar ko kuma lisha ta zama biyar to hukuncinshi anan ya yi sujjadar ba’adiyyah domin ya yi kari. Haka mutumin da ya kara sujjada a raka’a ta zama uku ko ya kara ruku’i ya zama biyu, amma da mantuwa shi ma ba’adiyyah zai yi. Wanda ya yi Magana a cikin sallah da mantuwa shima ba’adiyyah zai yi, ko ya sallame daga raka’a biyu da mantuwa, saida ya sallame ya tuna to anan sai ya ciko ragowar raka’o’in sannan ya yi ba’adiyyah. Wanda ya karanta surori biyu ko sa...

032. ABUBUWAN DA SUKE KAWO BA’ADIYYAH (2)

Gabatarwa: wannan shine tsagi na biyu na abubuwan da suke janyo ba’adiyyah a cikin sallah, ta fatan zamu kara kusantar malamai. Kokwanto: Idan mutum ya yi kokwanton sallarshi ta cika ko bata cika ba sai ya kawo abinda ya yi kokwanton sannan ba’adiyyah, misali; Idan ya yi kokwanton shin ya yi sujjadar ta cika ko bata cika ba, sai ka cika sannan ka yi ba’adiyyah. Idan mutum ya yi kokwanton wannan raka’ar itace ta hudu ko itace ta uku sai ya barta itace tau kun sai ya kawo cikon ta hudun sannan ya yi ba’adiyyah. Mutum mai yawan wasuwasi to abinda da ake so daga gareshi shine yabar wasuwasin ya kakkabeshi daga zuciyarsa ba zai kawo abinda ya yi kokwanton akanshi ba, sai bayan ya sallame sai ya yi ba’adiyyah, shin kokwanton akan karine ko akan ragi. Wannan yana nuna mana mafita daga mutanan da suke da yawan kokwanto da wasuwasi, Allah ya yaye musu mu kuma ya tsaremu, amin. Idan mutum ya yi shakkun yana da hadasi ko bai da shi? Sannan sai ya dan yi tunani kadan sai kuma ya samu tabbas ...

025- SUNNONIN SALLAH

025- SUNNONIN SALLAH Shinfida: Su sunnonin sallah su ne ke biye da farillan sallah wurin matsayi a cikin sallah, saboda haka kamar yadda bai kamata ka yi wasa da farillan sallah ba to haka yake bai kamata ka yi wasa da sunnonin sallah ba. Wasu da zarar sun ji ance abu kaza sunna ne to basa daukan shi da girma domin suna ganin rashin sa ba zai hana musu sallah ba, alhali kuwa wannan kuskurene mai girman gaske, ai ko ba’a sallah ba duk abinda ka ji an ce sunnane to bai kamata ka yi wasa da shiba. Su wadannan sunnoni na sallah kamar yadda bayani ya gabata matsayinsu baikai na farilla ba domin idan ka bar farilla daya a raka’a sai dai ka ajiye wannan raka’ar ka kawo wata makwafinta kamar yadda bayanai za su zo da izinin Allah a lokacin bayani kan kabaliyyah da ba’adiyya. Kennan su sunnonin sallah ba haka bane, idan mutum ya cika su to sallar shit a cika, idan ko bai cika su ba to sallar shi bata cika ba ko da ko ba zai sake ta ba. Saidai su sunnonin sallah asune ake samun damar kyara...

Quran Recitation by Al-Ghamdi post by MUstapha danjuma

Quran Recitation by Al-Ghamdi post by MUstapha danjuma Bismillah ir-Rahman ir-Rahim. The FreeQuranMP3.com crew humbly seeks the pleasure of Allah Subhanahu Wa Ta'ala by providing you with the complete Quran recitation by Sheikh Sa'ad Al-Ghamdi. Download, listen and share with others, insha'Allah. Quran Mp3 files CLICK  HERE  TO DOWNLOAD completely QUR'AN BY AL Post by IRSHAD group of school islamiyya students 1. Musa Muhammad Muktar 2.Mustapha Danjuma 3. Haruna Muhammad 4. Muhammad Auwal 5. Muktar Usman 6. Fadeela Abdulkareem 7. Munira Muhammad 8. Haleemah Umar Fo  booking call Malama ummi 08065771988

FULL Quran Recitation by As-SudaisAs-Sudais Post by Musa El muktar

FULL Quran Recitation by As-SudaisAs-Sudais Post by Musa muhammad Bismillah ir-Rahman ir-Rahim. The FreeQuranMP3.com crew humbly seeks the pleasure of Allah Subhanahu Wa Ta’ala by providing you with the complete Quran recitation by Sheikh Abdur-Rahman As-Sudais. Download, listen and share with others, insha’Allah. Quran Mp3 files Click  HERE  To Downloaded complete Qur'an Post by IRSHAD group of school islamiyya students 1. Musa Muhammad Muktar 2.Mustapha Danjuma 3. Haruna Muhammad 4. Muhammad Auwal 5. Muktar Usman 6. Fadeela Abdulkareem 7. Munira Muhammad 8. Haleemah Umar Fo  booking call Malama ummi 08065771988

YADDA AKE WANKAN JANABA, HAILA, BIKI DA DAI SAURAN SU

YADDA AKE WANKAN JANABA, HAILA, BIKI DA DAI SAURAN SU. Daga Marigayi Sheikh Jafar Mahmud Adam Kano.Wankan Janaba yana da siffa guda biyu: Akwai 'siffatul ijza' (ta wadatar), kuma wacce ake kira 'siffatu kamal' (ta kamala).Wankan Janaba a siffar sa ta kamala shi ne: Idan kazo zaka yi ko za kiyi wanka ga ruwa a gabanka. Farkon abin da zaka fara yi shi ne:zaka karkato bakin mazubin ruwanka, ka wanke hannunka sau uku, sannan sai ka tsoma hannu a cikin ruwan sai ka debo ka wanke gaban ka ، a dai-dai lokacin da zaka wanke gaban ka a lokacin zaka kulla niyya ta wankan janaba (Ko waninsa) wanda yake wajibi ne, idan ka wanke gabanka ma'ana kayi tsarki kenan، to daga nan kuma sai kayialwala irin yanda kake alwala ta sallah, abin da duk kake a alwala ta sallah zakayi sai abu daya shi ne wanke kafafu to wannan zaka kyale shi ba zaka yi shiba, to daga nan sai ka tsoma hannunka guda biyua cikin ruwan ba tare da ka debo ruwa ba sai ka murmurza kanka saboda kowane gashi da ya ...

TAUHIDI (kadaita Allah)

Tauheed shine kadaita Allah a wajen bauta Dasunan Allah Mai Rahama Mai Jinkai TAUHIDI (kad'aita Allah) Shine kadaita Allah a cikin Bauta shi kadai batare da hadashi da wani ba, kuma shine Addinin da aka aiko Annabawa dashi gaba dayaAllah yakara masu Aminci, kuma Allah baze karbi wani Addini ba inba shiba, kuma baya karban Ayyukan bayi se dashi, domin shine Asalin da ake gina Addini akanshi, kuma duk sanda aka rasashi to aikin bawa baze amfane shiba. KARKASUWAN TAUHIDI Tauhidi yakasu zuwa kashi uku (3): 1. Tauhidin Rububiyyah (Reno) Shine kudurce cewa Allah, shine wanda ya halicci, dukkan halittu, yake azurtasu, kuma wannan Nau’i na Tauhidi babu wanda yake musunshi, har mushrikan farko sun tabbatar dashi, kamar su Abu Jahal, fir’auma ne kawai wanda yatabayin musun babu ubangiji, sun kasance suna shedawa cewa Allah shine wanda yake halitta, yake gudanar dakomai dake cikin duniya, shike rayawa, yake kashewa, Allah madaukakin Sarki yace “Kuma idan kuka tambayesu wanene wanda ...