Skip to main content

ABUBUWAN DASUKE BATA SALLAH BY FADEELA ABDUL KAREEM

Gabatarwa: Anan za’a kawo bayanaine na kadan daga cikin abubuwan da suke bata sallah ta yadda ba abinda ya ragewa mutum saidai ya sake wannan sallar, kabaliyyah ko ba’adiyyah basa magance matsalar da aka samu. Wannan ya nuna cewa lalle wannan maudu’i yanada matukar muhimmanci ga kowanne mutum musulmi. Ga kadan daga cikinsu:
1. Dariya: Dariya tana daga cikin manyan abubuwan da suke bata sallah ko an yi ta da gangan ne ko kuma da mantuwa wato ya manta cewar shi yana sallah, ai ba mai dariya a sallah sai rafkananne, saboda haka mu sani sallah ba karamar ibada bace ba’a dariya a cikin sallah kuma duk wanda ya yi dariya a cikin sallah to sallar shi ta baci sai ya sake ta.
2. Kari Dagangan: Idan mutum ya yi Karin raka’a ko ruku’u ko sujjada dagangan to anan sallarsa ta baci, domin kuma ya dauki addinin da wasa da wargi, wanda yake addinin musulunci bai ginu akan hakaba. Amma idan rafkana ya yi har ya yi kari to anan sallar shi bata baciba bayanan yadda zai gyra za su zo ababin kabaliyyah da ba’adiyyah idan Allah ya kaimu.
3. Ci Ko Sha: Duk mutumin da ya ci ko ya sha yana cikin sallah to sallar shi ta baci, domin da zarar ka yi kabbarar harama to ka shiga cikin haramin sallah duk wadannan sun haramta a gareka, saboda haka duk wanda ya ci ko ya sha yana cikin sallah to sallar shi ta baci sai ya saketa.
4. Magana Dagangan: Idan mutum ya yi Magana da gangan kuma maganar bata gyaran sallah bace to sallar shi ta baci. Kenan idan ba dagangan ya yi maganarba to sallar shi nanan, amma zai yi ba’adiyyah domin ya yi kari a cikin sallah. Haka kuma idan ya yi maganarne dagangan amma ya yi ta ne domin gyaran sallah to sallar shi nanan, misali liman ne sallah ta rikice masa ya rasa yadda zai yi sai yace ‘Ina muke ? ko ‘Raka’a nawa muka yi ?’ anan maganar da ya yi ta halatta kuma maganar wanda ba yashi amsa ita ta halatta domin an yi ne saboda gyaran sallah.
Amma idan maganar ta yi yawa to sallar zata baci, saboda haka da zarar wani ya bada amsa to kais a ka yi shiru, domin ba wata majalisa za’a budeba da za’a ce kowa sai ya fadi albarkacin bakinsa.
5. Hadasi: Da zarar mutum yana cikin sallah sai ya yi hadasi to sallar shi t abaci sai ya sake, shi kuma hadasi shine; dukkan abinda yake fita ta mafita guda biyun nan al’aurar gaba da dubura, kamar; tusa, fitsari, maziyyi…’’ .
6. Tuna Sallar Baya: Idan mutum yana cikin sallah sai ya tuna ai bai yi sallar da ta wuceba to wannan sallar da yake yi ta baci, misali yana cikin sallar la’asar sai ya tuna ai bai yi azaharba to anan la’asardin ta baci. To maye abin yi ? abin yi anan idan shi kadai yake sallar sai ya karo raka’a su zama biyu sai ya sallame ya maida su nafila kenan, sannan ya kawo wacce ta wucedin sai kuma ya maida wannan da cikakkun raka’o’inta, idan kuma yana bayan limanne sai ya ci gaba da bin liman din, idan an sallame sai ya kawo wacce ta wucedin sannan ya maida wannan da ya yi tare da liman. Amma idan bai tuna da sallar da ta wuce ba sai bayan da ya kammala sallar da ta biyo bayanta to anan wacce ta wuce kawai zai kawo ita kadai ba zai sake wacce ta biyo bayan nata ba.
7. Kara Kwatankwacin Sallar: Idan mutum ya yi rakannuwa har ya kara kwatankwacin raka’o’in wannan sallar to sallar ta baci, misalin sallah mai ra’a biyu ya karo biyu su zama hudu da rafkannuwa ai sallar ta baci sai an sake, ko masu raka’o’I hudu ya kara wasu hudun suka zama takwas ko mai uku ya karo wasu ukun suka zama shida to anan sallolin sun baci. Wannan fa ana bayanine idan da rafkannuwane domin abinda da aka kara ba zai yiwu a yi kabaliyyah ko ba’adiyyah ba, amma Karin raka’a guda da ganganci yana bata sallah, saboda haka a banbance.
Kammalawa: Wadannan kadan kenan daga cikin abubuwan da suke bata sallah wanda hakan yake zama wajibi sai an sake ta, da fatan mun karu, kuma Allah ya karba mana ibadummu, amin.

Post by IRSHAD group of school islamiyya students

1. Musa Muhammad Muktar
2.Mustapha Danjuma
3. Haruna Muhammad
4. Muhammad Auwal
5. Muktar Usman
6. Fadeela Abdulkareem
7. Munira Muhammad
8. Haleemah Umar

Fo  booking call Malama ummi 08065771988

Comments

Popular posts from this blog

YADDA AKE WANKAN JANABA, HAILA, BIKI DA DAI SAURAN SU

YADDA AKE WANKAN JANABA, HAILA, BIKI DA DAI SAURAN SU. Daga Marigayi Sheikh Jafar Mahmud Adam Kano.Wankan Janaba yana da siffa guda biyu: Akwai 'siffatul ijza' (ta wadatar), kuma wacce ake kira 'siffatu kamal' (ta kamala).Wankan Janaba a siffar sa ta kamala shi ne: Idan kazo zaka yi ko za kiyi wanka ga ruwa a gabanka. Farkon abin da zaka fara yi shi ne:zaka karkato bakin mazubin ruwanka, ka wanke hannunka sau uku, sannan sai ka tsoma hannu a cikin ruwan sai ka debo ka wanke gaban ka ، a dai-dai lokacin da zaka wanke gaban ka a lokacin zaka kulla niyya ta wankan janaba (Ko waninsa) wanda yake wajibi ne, idan ka wanke gabanka ma'ana kayi tsarki kenan، to daga nan kuma sai kayialwala irin yanda kake alwala ta sallah, abin da duk kake a alwala ta sallah zakayi sai abu daya shi ne wanke kafafu to wannan zaka kyale shi ba zaka yi shiba, to daga nan sai ka tsoma hannunka guda biyua cikin ruwan ba tare da ka debo ruwa ba sai ka murmurza kanka saboda kowane gashi da ya ...

NASIHA AKAN WANDA BAYA SALLAH KO YAKE WASA DA ITA BY MUSA MUHAMMAD MUKTAR

Tsoratarwa Akan Wanda Ba Ya Yin Sallah Ko Yake Wasa Da Ita Tsoratarwa Akan Wanda Ba Ya Yin Sallah Ko Yake Wasa Da Ita Sallah daya ce daga cikin rukunnan musulinci guda biyar wanda musuluncin bawa ba ya cika har ya tsayar da ita. Mazon Allah SAW yana cewa: "Tsakanin mutum da tsakanin shirka da kafirci, shine barin Sallah. (Muslim). Manzon Allah SAW yana cewa: "Alkawarin da yake tsakanin mu da kafurai ita ce sallah, dukkan wanda ya bar sallah to ya kafirta). @ ﺳﻨﻦ ﺍﻟﺘّﺮﻣﺬﻱ ﻭﻏﻴﺮﻩ . Imam Tirmizy ya ruwaito daga Abdillahi bn Shaqeeq al'ukaily yace: "Sahabban Annabi Muhammad s.a.w basu ganin barin aiki wani aiki kafircine inbanda sallah". @ ﺍﻟﺘّﺮﻣﺬﻱ. Wato sun hadu akan dukkan wanda ya bar sallah kafiri ne. Manzon Allah s.a.w yana cewa: "Farkon abinda za'ayi wa bawa hisabi akansa na aiyukansa shine sallah, idan ta cika ta yi kyau ya tsira kuma ya rabauta, idan ba ta yi kyau ba kuma bata cika ba ya halaka ya tabe, idan an sami nakasa a cikin f...

025- SUNNONIN SALLAH

025- SUNNONIN SALLAH Shinfida: Su sunnonin sallah su ne ke biye da farillan sallah wurin matsayi a cikin sallah, saboda haka kamar yadda bai kamata ka yi wasa da farillan sallah ba to haka yake bai kamata ka yi wasa da sunnonin sallah ba. Wasu da zarar sun ji ance abu kaza sunna ne to basa daukan shi da girma domin suna ganin rashin sa ba zai hana musu sallah ba, alhali kuwa wannan kuskurene mai girman gaske, ai ko ba’a sallah ba duk abinda ka ji an ce sunnane to bai kamata ka yi wasa da shiba. Su wadannan sunnoni na sallah kamar yadda bayani ya gabata matsayinsu baikai na farilla ba domin idan ka bar farilla daya a raka’a sai dai ka ajiye wannan raka’ar ka kawo wata makwafinta kamar yadda bayanai za su zo da izinin Allah a lokacin bayani kan kabaliyyah da ba’adiyya. Kennan su sunnonin sallah ba haka bane, idan mutum ya cika su to sallar shit a cika, idan ko bai cika su ba to sallar shi bata cika ba ko da ko ba zai sake ta ba. Saidai su sunnonin sallah asune ake samun damar kyara...