Skip to main content

Posts

Matsayin Sallah Da Hukuncinta BY MUSA MUHAMMAD MUKTAR

Matsayin Sallah Da Hukuncinta Bayani Mece ce Sallah Ma’anar kalmar sallah a larabce Ita ce «Addu’a» Ma’anar Sallah a shari’ance Ita ce bautawa Allah da zantuka da ayyuka kevantattu, waxanda ake buxe su da kabbara, a rufe su da sallama. Matsayin Sallah A Musulunci 1 – Sallah ita ce rukuni na biyu a rukunan musulunci, Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “An gina musulunci a bisa ginshiqai guda biyar, shaida wa babu abin bauta wa bisa cancanta sai Allah, kuma Muhammad bawansa ne Manzonsa ne, da tsayar da sallah…..” [Bukhari da Muslim ne suka rawaito shi] . 2 – Sallah ita ce mafi falalar ayyuka, Manzon Allah (S.A.W) ya ce, “Mafi falalar ayyuka sallah a farkon lokacinta” [ Tirmizi ne ya rawaito shi] . 3 – Sallah ce mararraba tsakanin musulunci da kafirci, Annabi (S.A.W) ya ce, “Haqiqa tsakanin mutum da shirka da kafirci barin sallah” [Muslim ne ya rawaito shi] . 4 – Sallah ita ce ginshiqin musulunci, a kanta ne – bayan tauhidi – aka gina musulunci, Annabi yana cewa “Kan wannan ...
Recent posts

NASIHA AKAN WANDA BAYA SALLAH KO YAKE WASA DA ITA BY MUSA MUHAMMAD MUKTAR

Tsoratarwa Akan Wanda Ba Ya Yin Sallah Ko Yake Wasa Da Ita Tsoratarwa Akan Wanda Ba Ya Yin Sallah Ko Yake Wasa Da Ita Sallah daya ce daga cikin rukunnan musulinci guda biyar wanda musuluncin bawa ba ya cika har ya tsayar da ita. Mazon Allah SAW yana cewa: "Tsakanin mutum da tsakanin shirka da kafirci, shine barin Sallah. (Muslim). Manzon Allah SAW yana cewa: "Alkawarin da yake tsakanin mu da kafurai ita ce sallah, dukkan wanda ya bar sallah to ya kafirta). @ ﺳﻨﻦ ﺍﻟﺘّﺮﻣﺬﻱ ﻭﻏﻴﺮﻩ . Imam Tirmizy ya ruwaito daga Abdillahi bn Shaqeeq al'ukaily yace: "Sahabban Annabi Muhammad s.a.w basu ganin barin aiki wani aiki kafircine inbanda sallah". @ ﺍﻟﺘّﺮﻣﺬﻱ. Wato sun hadu akan dukkan wanda ya bar sallah kafiri ne. Manzon Allah s.a.w yana cewa: "Farkon abinda za'ayi wa bawa hisabi akansa na aiyukansa shine sallah, idan ta cika ta yi kyau ya tsira kuma ya rabauta, idan ba ta yi kyau ba kuma bata cika ba ya halaka ya tabe, idan an sami nakasa a cikin f...

HASSADA MUGUN CIWO , ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA ,( Imam Aliyu Indabawa )

HASSADA MUGUN CIWO , ANIYARKA TABI KA ABDULJABBAR KA SANI HALIFA QARIBULLAH YAFI KARFINKA ,( Imam Aliyu Indabawa ) Wannan da kuke gani shine Dr kalifa qaribullah nasiru kabara, wanda ya kasance shine halifan dariqar qadiriyya, kuma muna girmama shi saboda halayensa na kawaici da sanin ya kamata, sai Allah ya jarrabe shi da wani taqadarin kani wanda ya addabe shi da hassada kullum cikin zaginsa yakeyi yana kushe shi yana aibata shi, . Asali abinda yasa yake masa wannan hassadar shine saboda halifa qaribullahi Allah yayi masa ni'imomi da baiwarwaki wanda shi kanin nasa bashi dasu, yafi shi duk wani abu da ake so, ta bangaren daukaka, da Ilmi da 'yaya da kudi da magoya baya da manyan mutane Sarakuna, uwa uba kuma yana da hankali wanda shi kanin nasa yayi rashinsa, . Sannan ga mukamin Halifa da yake rike dashi wanda shine yafi komai kona masa zuciya da motsa masa hassada, saboda shi a tunaninsa ai shine yafi cancanta daya gaji mahaifinsa ya zama halifan qadiriya saboda tunan...

HUDUBAR JUMU' A DAGA MASALLACIN JUMU' A NA IHYA ' US SUNNAH DAKE KOFAR NASSARAWA KANO AUDIO MP 3 ( Basheer Journalist Sharfadi )

HUDUBAR JUMU' A DAGA MASALLACIN JUMU' A NA IHYA ' US SUNNAH DAKE KOFAR NASSARAWA KANO AUDIO MP 3 ( Basheer Journalist Sharfadi ) -A yau Jumu'a 21/Shawwal/1436. Wadda tayi dai-dai da 07/Aug/2015. Babban Limamin Masallacin Jumu'a na Ihya'us-Sunnah dake Kofar Nassarawa a Karamar Hukumar Birnin Kano da Kewaye. Sheik Dr. Muhammad Sani Ashir Kano Shine Ya Jagoranci Huduba da Sallah a Masallacin. -Dr. Sani Ashir Kano ya fara gabatar da Hudubar sa ne da misalin Karfe 12:30 na rana a Masallacin. Inda aka tayar da Sallah da Karfe 01:05 na rana Bayan Kammala Hudubar. Babban Limamin Yayi Hudubar ne Akan Tauhidi wato Kadaita Allah da yi masa bauta shi kadai. -An gudanar da Sallar cikin nutsuwa da kwanciyar Hankali Kamar Yadda aka saba tare da Gudummuwar Yan agaji wajen bayar da da kyakykyawar Kulawa Domin ganin ayyuka sun gudana kamar yadda aka saba. -Kar dai na cikaku da surutu Danna Kasa Domin Sauraron Hudubar daga Bakin Dr.:

027- ABUBUWAN DA BA’A YIN SU A SALLAH

Shinfida: Su wadanann abubuwa su malamai suke kira ‘Makruhatus Salah’ wato abubuwan da ba’a so ayi su a cikin sallah, domin yinsu yana matukar ragewa mutum ladan sallarsa, dudda sallar bat abaci ba ta yadda za’a ce sai ya sake, kuma ba zai yi kabaliyyah ko ba’adiyyah saboda ya yisu ba, saboda haka sai a kiyaye kada mutum ya yi wasa da sallarsa, Hssan dan Atiyyah yake cew: ‘’Lalle mutane biyu za su iya kasancewa a cikin sallah guda, amma tazarar dake tsakaninsu na falala ya fi nisan sama da kasa’’. Lalle wannan ba karamar Magana bace indai har mutane biyu za su kasance a sallah guda bayan limami guda amma banbancin dake tsakaninsu ya dara tazarar dake tsakanin sama da kasa, to kan lalle bakaramin banbanci bane, sannan tambaya anan itace: Me ya janyo wannan banbanci na falala?. Natsuwa kwantar da hankali kankar-da-kai, da kuma sanin me mutum yake yi da nisantar abinda ba’a so mutum ya yi a cikin sallah, wadannan kadanne daga cikin abubuwan da za su banbanta falalar masallata, ga kadan...

ABUBUWAN DASUKE BATA SALLAH BY FADEELA ABDUL KAREEM

Gabatarwa: Anan za’a kawo bayanaine na kadan daga cikin abubuwan da suke bata sallah ta yadda ba abinda ya ragewa mutum saidai ya sake wannan sallar, kabaliyyah ko ba’adiyyah basa magance matsalar da aka samu. Wannan ya nuna cewa lalle wannan maudu’i yanada matukar muhimmanci ga kowanne mutum musulmi. Ga kadan daga cikinsu: 1. Dariya: Dariya tana daga cikin manyan abubuwan da suke bata sallah ko an yi ta da gangan ne ko kuma da mantuwa wato ya manta cewar shi yana sallah, ai ba mai dariya a sallah sai rafkananne, saboda haka mu sani sallah ba karamar ibada bace ba’a dariya a cikin sallah kuma duk wanda ya yi dariya a cikin sallah to sallar shi ta baci sai ya sake ta. 2. Kari Dagangan: Idan mutum ya yi Karin raka’a ko ruku’u ko sujjada dagangan to anan sallarsa ta baci, domin kuma ya dauki addinin da wasa da wargi, wanda yake addinin musulunci bai ginu akan hakaba. Amma idan rafkana ya yi har ya yi kari to anan sallar shi bata baciba bayanan yadda zai gyra za su zo ababin kabaliyyah ...

029- SUJJADAR RAFKANNUWA (KABALIYYAH DA BA’ADIYYAH) ›

Gabatarwa: Ayanzu da izinin Allah muna son mu kawo bayanaine da suka shafi sujjar rafkannuwa wacce ake kira Kabaliyyah ko ba’adiyya da fatan Allah ya anfanar da mu da wadannan bayanai, kuma ya sanya ya zama sanadiyyar tsira duniya da lahira. Wadannan bayanai za su kunshi me ake nufi da sujjadar rafkannuwa ko mecece kabaliyyah sannan mecece ba’adiyyah, sannan a kawo bayanai na abinda ke sabbaba wadannan sujjadu. Sujjadar Rafkannuwa: Sujjadune guda biyu da mutum yake yinsu bayan ya kammala sallah kafin sallama ko bayan sallama saboda kari ko ragi ko kokwanto da ya yi a cikin sallah. Wannan ta’arifi da ya gabata ya fayyace mana me ake nufi da sujjadar rafkannuwa kuma ya yi bayanin abinda yasa ake yenta da kuma lokacin da ake yenta da kuma dadi nawa ake yi. Kabaliyyah : Sune sujjadu biyu da ake yi bayan tahiyyah kafin sallama, kasancewa ana yinta kafin sallama shi yasa ake kiranta kabaliyyah wato ‘Kabals Salam’. Ba’adiyyah: Sune sujjadu biyu da ake yi bayan an sallame daga sallah, sa...